Ziyarar Babban Hafsan Sojoji A Katsina: Radda Ya Nemi Ƙara Ɗaukar Mataki Kan Matsalar Tsaro

top-news

Zaharaddeen Ishaq Abubakar,Katsina Times - 6 ga Satumba, 2024 - 


Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bukaci sojojin Najeriya da su kara daukar matakai domin kawo karshen matsalar tsaro a jihar yayin wani taro da Shugaban Hafsan Sojojin Kasa, Laftanar Janar Taoreed A. Lagbaja.

Gwamna Radda ya nemi daukar mataki cikin gaggawa lokacin samun kiran neman taimako, inda ya jaddada muhimmancin yin hanzari wajen ceto al'umma yayin hare-hare.

Ya yaba da jajircewar rundunar sojan Najeriya wajen tunkarar kalubalen tsaro, tare da haskaka kyakkyawan sakamakon hadin gwiwar jami’an tsaro.

Sai dai, ya yi kira da a kara daukar matakan da za su tabbatar da cewa manoma na iya jigilar amfanin gonarsu lafiya zuwa gida.

Laftanar Janar Lagbaja ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa za a iya shawo kan kalubalen tsaro ta hanyar hadin gwiwa, sannan ya yabawa Gwamna Radda bisa goyon bayansa ga rundunar soji a jihar.

Shugaban sojan ya roki goyon bayan gwamnatin jihar wajen wayar da kan jama’a game da muhimmancin taimakawa da hadin kai da sojoji wajen magance matsalolin tsaro yadda ya kamata.

Hoto; KSGH

NNPC Advert